Toggle menu
24K
666
183
158.3K
HausaDictionary.com | Hausa English Translations
Toggle preferences menu
Toggle personal menu
Not logged in
Your IP address will be publicly visible if you make any edits.

Quran/3/Rijayar Lemo Tafsir2: Difference between revisions

From HausaDictionary.com | Hausa English Translations
No edit summary
No edit summary
Line 137: Line 137:
# Maƙiyanmu ba za su gaji da shirya mana makirci da sharri ba; to maganin wannan kawai shi ne haƙuri da taƙawa. Mu yi haƙuri wajen aikata duk wani umarni da aka ba mu, da guje wa duk wani abu da aka hana mu. Duk wanda ya yi haƙuri ya ji tsoron Allah; to yana ƙarƙashin kulawar Ubangijinsa, babu makircin da zai cutar da shi.
# Maƙiyanmu ba za su gaji da shirya mana makirci da sharri ba; to maganin wannan kawai shi ne haƙuri da taƙawa. Mu yi haƙuri wajen aikata duk wani umarni da aka ba mu, da guje wa duk wani abu da aka hana mu. Duk wanda ya yi haƙuri ya ji tsoron Allah; to yana ƙarƙashin kulawar Ubangijinsa, babu makircin da zai cutar da shi.
# A ƙarƙashin aya ta [[Quran/3/120|3:120]], malamai suka fitar da ƙa'ida game da maƙiyi, suka ce shi ne wanda yake farin ciki da abin da ya baƙanta maka, yake baƙin ciki da abin da ya faranta maka. When you ˹believers˺ are touched with good, they grieve; but when you are afflicted with evil, they rejoice. ˹Yet,˺ if you are patient and mindful ˹of Allah˺, their schemes will not harm you in the least. Surely Allah is Fully Aware of what they do.
# A ƙarƙashin aya ta [[Quran/3/120|3:120]], malamai suka fitar da ƙa'ida game da maƙiyi, suka ce shi ne wanda yake farin ciki da abin da ya baƙanta maka, yake baƙin ciki da abin da ya faranta maka. When you ˹believers˺ are touched with good, they grieve; but when you are afflicted with evil, they rejoice. ˹Yet,˺ if you are patient and mindful ˹of Allah˺, their schemes will not harm you in the least. Surely Allah is Fully Aware of what they do.
Tarjama Da Tafsirin ayoyin 121-129


== Tarjama Da Tafsirin ayoyin 121-129 ==
# Kuma ka tuna lokacin da ka yi sammako daga wajen iyalinka, ka je kana shirya wa muminai wuraren tsayuwarsu don yaƙi. Allah kuwa Mai ji ne, Masani. --[[Quran/3/121]]
# Kuma ka tuna lokacin da ka yi sammako daga wajen iyalinka, ka je kana shirya wa muminai wuraren tsayuwarsu don yaƙi. Allah kuwa Mai ji ne, Masani. --[[Quran/3/121]]
# Tuna lokacin da wadansu kungiyoyi guda biyu daga cikinku suka yi niyyar su ja da baya, amma Allah ne Majibincin lamarinsu. Sai muminai su dogara ga Allah kadai. --Quran/3/122
# Tuna lokacin da wadansu kungiyoyi guda biyu daga cikinku suka yi niyyar su ja da baya, amma Allah ne Majibincin lamarinsu. Sai muminai su dogara ga Allah kadai. --Quran/3/122
Line 196: Line 196:
#Bayanin irin kyakkyawar mu'amalar Manzon Allah SAW ga sahabbansa lokacin da suke fuskantar wata fargaba da tashin hankali. Annabi SAW yakan shigar musu da kyakkyawan fata a zukatansu, wanda hakan shi ne yakan dawo musu da kuzarinsu, ya tafiyar musu da bakin cikinsu da damuwarsu, ya sa su tashi tsaye domin aiki ba ja da baya.
#Bayanin irin kyakkyawar mu'amalar Manzon Allah SAW ga sahabbansa lokacin da suke fuskantar wata fargaba da tashin hankali. Annabi SAW yakan shigar musu da kyakkyawan fata a zukatansu, wanda hakan shi ne yakan dawo musu da kuzarinsu, ya tafiyar musu da bakin cikinsu da damuwarsu, ya sa su tashi tsaye domin aiki ba ja da baya.
#Sama ita ce mazaunin mala'iku, sai dai sau tari sukan sauko kasa da umarni Allah.
#Sama ita ce mazaunin mala'iku, sai dai sau tari sukan sauko kasa da umarni Allah.
#Allah yakan ba wa muminai nasara a kan kafirai,
#Allah yakan ba wa muminai nasara a kan kafirai, domin ya rage mugun iri, ba don ya halaka duk ilahirin kafirai ba. Saboda yana daga cikin hikimar Allah, ya bar imani da kfafirci su ci gaba da wanzuwa, suna ta qaruwa, domin tantance mumini na gaskiya da wanda ba na gaskiya ba.
#Cewar da Allah ya yi, al'amari ba a hannun Annabi yake ba, don haka ba ya halattun Ubangiji ba mallakinsa ne ba, don haka ba ya halatta mumini ya roke shi, ko ya nemi agajinsa da taimakonsa a kan abin da ba mai yin sa sai Allah, ballantana kuma wani waliyyi.
#Annabi SAW shi ma bawa ne na Allah, kuma har ya bar duniya yana karbar umarni da hani ne daga Allah. Da wannan ne za mu fahinci batan masu da'awar cewa, akwai wasu waliyyai da suke kaiwa matakin da sun fi karfin su karbi umarni ko hani daga Allah, ko kuma bawa ya kai wani matakin da shari'a take sauka daga kansa. Wannan kafirci ne, ba Musulunci ba.
#Allah yakan yi wa kafirai azabar da babu hannun wani Musulmi a ciki.
 
== '''Tarjama Da Tafsirin Aya Ta (130-132)''' ==
 
# Ya ku wadanda suka yi imani, kada ku ci riba ninki-ba-ninkin, kuma ku ji tsoron Allah don ku rabauta. --[[Quran/3/130]]
# Kuma
 
[[Category:Quran/3]]
[[Category:Quran/3]]

Revision as of 23:34, 13 August 2024

Quran/3 > Quran/3/Rijayar_Lemo_Tafsir > Quran/3/Rijayar_Lemo_Tafsir2

Tarjama Da Tafsirin ayoyin 100-101 na Surar Ali Imran

  1. Ya ku wadanda suka yi imani, idan kuka bi wani bangare na wadanda aka ba wa Littafi, to za su mayar da ku kafirai bayan imaninku. --Quran/3/100
  2. Ta yaya kuma za ku kafirce, ga shi kuwa ana karanta muku ayoyin Allah, kuma Manzonsa yana tare da ku? Duk kuwa wanda ya riki Allah, to hakika an shiryar da shi tafarki madaidaici. --Quran/3/101

A wadannan ayoyi Allah yana gargadin muminai da cewa, idan suka kuskura suka nuna biyayyarsu ga Yahudawa da Nasara, wadanda suke yi musu hassadar Alqur'ani da Allah ya ba su da falalar Musulunci; to tabbas za su raba su da imaninsu, su mayar da su kafirai suna ji suna gani. Amma Allah ya nuna cewa, da wahala kwarai muminai su yarda su koma kafirci bayan ga Alkur'ani nan kullum suna ji ana karanta musu ayoyinsa, sannan ga Manzon Allah nan a tsakaninsu, yana isar musu duk wani saƙo da aka saukar dominsu. Shi imani idan har ya ratsa ƙoƙon zuciya; to abu ne mai wuyar gaske a iya cire shi, sai dai wani iko na Allah.

Sannan Allah ya bayyana musu wata hanya wadda idan suka bi ta, za su tsare kawunansu daga fadawa ramin kafirci. Wannan hanya ita ce, rike Allah da dogaro da shi, domin shi ne madogara ta samun shiriya. Duk wanda ya koma ga Allah a cikin kowanne hali nasa, ya nemi mafaka a wurinsa, ya dogara da shi dogaro na gaskiya, ya rike addininsa; to hakika wannan an shiryar da shi ga hanya mikakkiya dodar, wadda babu karkata ko kadan a cikinta, ita ce za ta yi masa jagoranci har ta kai shi gidan Aljanna.

Daga wadannan ayoyi za mu fahimci abubuwa kamar haka:

  1. Gargadin Musulmi a kan su yi hattara wajen yarda da maganganun Yahudawa da Nasara da aiki da su, ko kwaikwayon wani tsari nasu na rayuwa, domin zukatansu cike suke da hassada da kullata ga Musulmi, a kullum suna tunanin hanyar da za su bi su raba Musulmi suka yi sakaci suka karbi tsare-tsarensu na rayuwa; to za su iya kai su ga halaka.
  2. Sanin falalar sahabban Manzon Allah SAW, ta kasancewarsa ya rayu dauke da shi, kuma ya zame musu ƙaƙƙarfar katanga mai kare su daga faɗawa kafirci ko karkace hanyar gaskiya. Wannan ba karamar falala ba ce ga sahabbai; babu wanda ya sami irinta cikin wannan al'umma sai su.
  3. Riƙo da littafin Allah da sunnar Annabi SAW shi ne babban abin da zai tsare mumini daga kauce wa hanyar Allah, ko fadawa cikin kafirci.
  4. Idan zaman Annabi SAW a cikin wannan al'umma ya ƙare lokacin rayuwarsa, to ai ayoyin Allah da sunnonin Annabinsa suna nan a tsakanin al'umma, kuma Musulmi a yau ana neman su da aiki da Alƙur'ani da sunna, kamar irin yadda aka nemi musulmin farko da hakan; don haka har yanzu hanyar samun kariya da tsari a fili take.

Tarjama Da Tafsirin ayoyin 102-109

  1. Ya ku waɗanda suka yi imani, ku yi taƙawa ga Allah haƙiƙanin taƙawa, kuma lalle kada ku mutu face kuna Musulmi. --Quran/3/102
  2. Kuma ku yi riƙo da igiyar Allah gaba ɗaya, kada kuma ku rarraba. Kuma ku tuna ni'imar Allah da Ya yi muku yayin da kuka zamo abokan gaban juna sai Ya hada tsakanin zukatanku, sai kuka zamo 'yan'uwan juna a sakamakon ni'imarsa, a da kuma kun kasance a kan gabar ramin wuta sai Ya tserar da ku daga gare ta. Kamar haka ne Allah Yake bayyana muku ayoyinsa don ko kwa shiriya. --Quran/3/103
  3. A cikinku lalle a sami wata al'umma wadanda suke kira zuwa ga alheri, kuma suke umarni da kyakkyawa, kuma suke yin hani daga mummuna. Wadannan su ne masu rabauta. --Quran/3/104
  4. Kuma kada ku kasance kamar wadanda suka rarrabu, kuma suka sassaba bayan hujjoji sun zo musu. Wadannan kuwa suna da azaba mai girma. --Quran/3/105
  5. Ranar da wadansu fuskoki za su yi fari, wadansu fuskokin kuma za su yi baki. Amma wadanda fuskokinsu suka yi baki, (ca a ce da su): "Shin ku ne kuka kafirce bayan imaninku? To ku dandani azaba, saboda kafircin da kuka kasance kuna yi." --Quran/3/106
  6. Amma wadanda fuskokinsu suka yi fari kuwa, to suna cikin rahamar Allah, suna masu dawwama a cikinta. --Quran/3/107
  7. Wadannan ayoyin Allah ne muke karanta maka su da gaskiya. Kuma Allah ba Ya nufin zalunci ga talikai. --Quran/3/108
  8. Kuma duk abin da yake cikin sammai da kasa na Allah ne. Kuma zuwa ga Allah ne ake mayar da duk al'amura. --Quran/3/109

A wadannan ayoyi, Allah SWT yana umartar bayinsa muminai da su ji tsoronsa gwargwadon ikonsu, sannan su ci gaba da rike wannan addini ƙam-ƙam har mutuwa ta zo musu. Kuma lalle su haɗa kansu, su zama abu guda a kan gaskiya, su taru su riƙe igiyar Allah, wadda ita ce Alƙur'anin da Manzo ya zo musu da shi da sunnarsa; kada su yarda su rarrabu.

An karbo daga Abu Huraira ya ce: Annabi ya ce:

"Lalle Allah ya yarje muku abubuwa uku (3), kuma ya ƙi muku abubuwa uku. Ya yarje muku da ku bauta masa, kuma kada ku haɗa komai da shi, kuma duk ilahirinku ku yi riƙo da igiyar Allah, kada ku rarrabu, kuma ya ƙi muku bin jita-jita da yawan tambaya da ɓarnata dukiya." [Muslim #1715]

Abu Huraira reported Allah's Messenger (ﷺ) as saying:

Verily Allah likes three things for you and He disapproves three things for you. He is pleased with you that you worship Him and associate nor anything with Him, that you hold fast the rope of Allah, and be not scattered; and He disapproves for you irrelevant talk, persistent questioning and the wasting of wealth. https://sunnah.com/muslim:1715a

Sannan Allah ya umarce su da su tuna ni'imarsa da ya yi musu lokacin da suka hadu a kan Musulunci, suka zama 'yan'uwan juna, bayan a da kafin zuwan Musulunci a rarrabe suke, suna gaba da fada da junansu a kan abin da bai taka kara ya karya ba, sai ga shi Allah ya haɗa zukatansu gaba ɗaya sun zama 'yan'uwa masu ƙaunar junansu, kamar yadda ya bayyana hakan a Suratul Anfali, aya ta 62-63.

Kuma Allah ya tunatar da su cewa, suna dab da fadawa ramin wuta, sai Allah ya ceto su, domin babu abin da ya rage musu su fada cikinta sai mutuwa idan har suna cikin wannan hali na kafirci. To kamar irin wannan bayani da ya yi musu filla-filla har suka fahimta; to haka yake fayyace musu sauran ayoyin nasa, don su zame musu fitilar gane hanyar shiriya da gaskiya.

Sannan Allah ya umarci bayinsa da cewa, lalle a sami wata kungiya daga cikinsu, wadanda za su dauki nauyin yin umarni da kyakkyawan aiki da hana mummuna a cikin al'umma; wannan shi ne maganin rabuwar kai a tsakaninsu. Domin duk al'ummar da take rayuwa kara-zube, kowa yana yin abin da ya ga dama, babu mai tsawata masa yayin da ya yi ba daidai ba, to wannan al'umma za ta rasa haduwar kai a tsakanin 'ya'yanta, domin soye-soyen zukatan mutane mabambanta ne. Allah ya bayyana cewa, wadanda suka siffantu da sifar nan ta umarni da kyakkyawan abu, da hana mummuna, su ne masu samun babban rabo a duniya da lahira.

An karbo daga Huzaifa dan Alyaman ya ce, Annabi SAW ya ce: "Na rantse da wanda rai na yake hannunsa, Wallahi, ko dai ku yi umarni da kyakkyawan aiki, ku hana mummuna, ko kuma ba da dadewa ba Allah ya aiko muku da wata ukuba daga gare shi, ku yi ta addu'a ya ki amsa muku!" [Ahmad #23349 da Tirmizi #2169].

Hudhaifah bin Al-Yaman narrated that the Prophet (s.a.w) said: "By the One in Whose Hand is my soul! Either you command good and forbid evil, or Allah will soon send upon you a punishment from Him, then you will call upon Him, but He will not respond to you." https://sunnah.com/tirmidhi:2169

Sai kuma Allah ya hana muminai rarrabuwa, kamar yadda Yahudu da Nasara a gabaninsu suka rarraba a addininsu, bayan hujjoji daga Allah, a ranar da fuskokin 'yan Aljanna za su yi fari, fuskokin 'yan wuta kuma su yi baki. Sai cikin zargi a ce wa masu bakaken fuskoki: "Shin ku ne kuka kafirce bayan imaninku? To ku dandani azaba saboda kafircinku." Amma masu fararen fuskoki, za su kasance ne a cikin rahamar Allah, tare da jin dadin da Allah ya tanadar musu a Aljanna na ni'imomi masu yawa, za su ci gaba da rayuwa a cikinsu har abada.

Sannan Allah ya tabbatar wa Annabinsa cewa; wadancan ayoyi da ya karanta masa su ne gaskiya, kuma tabbas Allah ba wanda yake zalunta cikin halittunsa. Duk abubuwan da suke cikin sammai, da wadanda suke kasa na Allah ne shi kadai, kuma duk al'amura gaba daya gare shi za a mayar da su ranar alkiyama, domin ya saka wa kowa aikin da ya yi; idan ya aikata alheri, ya ga alheri, idan kuwa sharri ya aikata, to ya ga sharri.

Daga wadannan ayoyi za mu fahimci abubuwa kamar haka:

  1. Wajibi a kan Musulmi su ƙanƙame ma addinin Musulunci, kar su rabu da shi har zuwa mutuwarsu.
  2. Wajibi ne Musulmi su hada kai su zama al'umma daya. Hanyar hada kan kuma ita ce rike shari'ar Allah, wadda take kunshe cikin Alkur'ani da sunnar Annabi. Sabananin haka kuma shi ne rarrabuwa, wadda take nufin rike bidi'o'i da son zuciya.
  3. Tunowa da ni'imomin Allah ga bayinsa, wadanda suka shafi addininsu ko rayuwarsu ta duniya, da gode wa Allah a kansu a zukata da harshe, wannan zai kara musu son Allah, sai shi kuma ya kara musu falalarsa da kyautarsa.
  4. Kira zuwa ga addinin Allah wani ginshiki ne na tabbatar da tsarin Allah a bayan kasa da kuma murkushe karya da barna da kawar da mummunan aiki da tabbatar da kyakkyawa. To masu irin wannan aiki su ne masu rabauta duniya da lahira.

Tarjama Da Tafsirin ayoyin 110-112

  1. Ku ne mafi alherin al'umma wadanda aka fitar ga mutane, kuna umarni da kyakkyawan aiki, kuma kuna hana mummuna, kuma kuna yin imani da Allah. Da a ce kuwa Ma'abota Littafi za su yi imani da ya fi alheri a gare su. A cikinsu akwai muminai, amma mafiya yawansu fasikai ne. --Quran/3/110
  2. Ba za su taba iya cutar da ku ba sai dai cutarwa kadan; kuma in da za su yake ku, sai sun juya muku baya, sannan ba za a taimake su ba. --Quran/3/111
  3. An hada su da kaskanci a duk inda aka same su, sai dai wadanda suke rike da wani alkawari daga Allah ko wani alkawari daga mutane, kuma sun dawo da wani fushi daga Allah, kuma an hada su da talauci. Hakan kuwa saboda sun kasance suna kafirce wa ayoyiin Allah, kuma suna kashe annabawa ba tare da wani hakki ba, hakan yana faruwa ne saboda sabo da suka yi, kuma sun kasance suna ketare iyaka.

A wadannan ayoyi, Allah yana magana da wadannan al'umma. Farkon wadanda suka shiga cikin wannan kiran, su ne sahabban Annabi, domin su ne farkon wadanda ayar ta yi magana da su. Wannan matsayi mai girma sun cancance shi ne saboda sun siffantu da yin umarni da kyakkyawan aiki da hani da mummuna da kuma imani da Allah. Wannan ne ya sanya suka tsere wa al'ummomin da suka gabace su.

Da a ce Yahudawa da Nasara sun yi imani da Annabi da abin da ya zo da shi daga Ubangijinsa, to da ya fi musu alheri. Sai dai wadanda suka yi imani a cikinsu 'yan kadan ne, da dama daga cikinsu sun ci gaba ne da zama a kan kangare wa Allah da Manzonsa SAW. Wannan shi zai hana su kaunaci muminai sai dai su yi ta gaba da su da kokarin cutar da su duk sanda suka sami dama. Amma dai duk yadda suka kai ga nuna musu kiyayya da kokarin cin zarafinsu, ba za su iya ba in banda cutarwa da fatar baki ba. Idan ma da fada zai hada su da muminai; to ba za su iya taɓuka komai ba sai dai su gudu, kuma ba za a taimaka musu ba, domin kuwa Allah ya hada su da kaskanci da wulakanci a duk inda suke a bayan kasa, ba sa samun nutsuwa da kwanciyar hankali, sai da wani alkawari daga Allah ko daga mutane. Sannan kuma sun cancanci fushin Allah, kuma ga alamun talauci sun bayyana a tare da su. Irin wannan sakamakon ya faru da su ne saboda kafirce wa ayoyin Allah da suke yi, da kuma kashe annabawa ba tare da wani laifi ba, sai don zalunci kawai. Kuma abin da ya kai su ga wannan hali na kafirci da kisa, shi ne sabon Allah da suke yi da ketare iyakokinsa da shari'arsa.

Daga wadannan ayoyi za mu fahimci abubuwa kamar haka:

  1. Ayar farko tana nuna falalar sahabban Annabi da fifikonsu a cikin wannan al'umma. Duk da cewa ayar ta hada har da sauran muminai wadanda suka zo bayan sahabbai, sai dai sahabban ne aka fara fuskanta da ita, shi ya sa suka fi cancanta da ita. Sannan siffar umarni da kyakkyawan aiki, da hana mummunan aiki da siffar umarni da kyakkyawan aiki, da hana mummunan aiki da siffar imani da Allah, duk sun fi bayyana tare da sahabbai fiye da sauran muminai da za su zo bayansu.
    An karbo daga Abdullahi dan Abbas ya ce,
    Manzon Allah ya ce: "Mafi alherin mutane su ne na ƙarnina, sannan wadanda suke bi musu, sannan wadanda suke bi musu..." [Bukhari #3651]
    The Prophet (ﷺ) said, "The best people are those living in my generation, and then those who will follow them, and then those who will follow the latter. Then there will come some people who will bear witness before taking oaths, and take oaths before bearing witness." (Ibrahim, a sub-narrator said, "They used to beat us for witnesses and covenants when we were still children.") https://sunnah.com/bukhari:3651
  2. Ya kamata al'ummar Musulmi su fahimci cewa, su ne fiyayyu a cikin duk wata al'umma da aka taba yi a bayan kasa, don su fahimci kimarsu da darajarsu, kuma su gane cewa, sun fito ne don su ja ragamar tafiyar wannan al'umma. Kuma nufin Allah shi ne alheri ya yi jagoranci a bayan kasa ba sharri ba, a bayan kasa, don haka ya kamata su zama koyaushe su ne masu bayarwa, ba masu karba ba. Kuma abin da za su bayar na akida da ilimi da halayya da tsarin rayuwa ya zama mai inganci ne.
  3. Fahimtar cewa umarni da kyakkyawan aiki da hana mummunan aiki abu ne mai girman matsayi a addinin Musulunci, domin shi ne tubalin ginin fifikon wannan al'umma a kan sauran al'ummomi.
  4. Himmatuwa da samar da ingantaccen imani da Allah a zuciya, domin sai da shi ne za a yi umarni da kyakkyawa, a hana mummuna, saboda shi ne sahihin ma'auni na tantance abu mai kyau da mummuna.
  5. Fifita wannan al'umma da Allah ya yi a kan sauran al'ummomi, saboda siffantuwarsu ne da umarni da kyakkyawa da hani da mummuna. Hakan yana nuna wannan siffar ba za ta yanke ba a cikin al'ummar.
  6. Allah ya gabatar da ambaton umarni da kyakkyawan aiki da hana mummunan aiki, saboda dalilai kamar haka:
  • Domin nuna falalar umarni da kyakkyawan aiki da hani da mummunan aiki.
  • Kasancewar ana magana ne a kan fifita wannan al'umma a kan dukkan al'ummomi, muminansu da kafiransu, shi ya sa aka ambaci sifar da kowa ya yarda mai kyau ce.
  • Kuma domin kasancewar umarni da kyakkyawan aiki da hani da mummuna yana matsayin garkuwa mai kare imani, sai aka fara faɗar sa da farko, domin makarin kowane abu ana gabatar da shi ne.
  • Hakanan akwai shaguɓe ga Ma'abota Littafi waɗanda suke da'awar sun yi imani, amma sun kasa tsayawa su yi umarni da kyakkyawan aiki su yi hani da mummuna.
  • Kuma don a nuna cewa wannan al'umma sun tsaya a kan wannan aiki ne saboda sun yi imani da Allah da bayyana addininsa a fili.

Tarjama Da Tafsirin ayoyin 113-115

  1. Ba dukansu ne suka zama daya ba. Cikin Ma'abota Littafi akwai al'umma tsayayya, suna karanta Littafin Allah a cikin dare alhalin suna sujada. --Quran/3/113
  2. Suna yin imani da Allah da ranar karshe, kuma suna umarni da kyakkyawan aiki, kuma suna hana mummuna, kuma suna hanzari wajen ayyukan alheri, wadannan kuwa suna cikin salihan bayi.
  3. Kuma duk abin da suka aikata na alheri, to ba za a hana musu ladansa ba. Kuma Allah Yana sane da masu taqawa.

Bayan Allah ya ambaci kungiyar fasikai daga Ma'abota Littafi, sai kuma a wadannan ayoyi ya bayyana cewa, ba dukkansu suka taru suka zama daya ba; a cikinsu akwai mutanen kirki, wadanda Allah ya shirye su suka musulunta, suka rike gaskiya, suna kuma karanta littafin Allah a cikin sallolinsu na dare, kuma suna yin imani da Allah da ranar lahira. Kuma ba su tsaya ga gyara zukatansu su kadai ba; suna yin nasu kokarin su gyara wasu ta hanyar umartar su da kyawawan ayyuka da hana su aikata munana suna kuma gaggawa wajen aikata ayyukan alheri. Irin wadannan mutane su ne mutanen kirki salihai, kuma duk wani aikin alheri da za su yi ba za a haramta musu ladansa ba a wajen Allah. Allah kuma ya san masu taqawa, yana ganin ayyukansu, kuma zai yi musu kyakkyawan sakamako a lahira.

Daga wadannan ayoyi za mu fahimci abubuwa kamar haka:

  1. Adalcin Allah. Bayan ya soki kungiyar Ma'abota Littafi masu kafirce wa Allah, da kashe annabawa ba da wani hakki ba. To don kada wani ya zaci duka haka halayensu suke, sai Allah ya bayyana cewa, a cikinsu akwai na kirki, masu halaye da yake so. To haka ya wajaba a rika yin adalci, ko da kuwa da wanda ake sabani da shi ne.
  2. Muhimmancin yawan karatun Alkur'ani cikin dare. Kuma sallar nafila ta dare ta fi ta rana saboda mai salla a lokacin ya fi tara hankalinsa wuri guda, domin babu wani abu da zai dauki hankalinsa kamar da rana, kuma akwai kauce wa riya a cikinta, da sauran wasu abubuwa masu rushe ayyuka, ko su nakasa su.
  3. Muhimmancin umarni da kyakkyawan aiki, da hani da mummuna. Saboda muminai bayan sun inganta kansu da imani, kuma suna kokarin inganta wasu ta hanyar umartar su da kyawawan ayyuka, da kuma hana su munana, wannan kuwa shi ne matukar kamala.
  4. An gabatar da ambaton karatun Alkur'ani a kan imani da Allah da ranar lahira, domin bai yiwuwa mutum ya yi imani da abu, sai bayan ya san shi, don haka idan sun karanta ayoyin Allah, sai su san mene ne ranar lahira, sannan su yi imani da ita.

Tarjama Da Tafsirin ayoyin 116-117

  1. Lalle wadanda suka kafirta, dukiyoyinsu da 'ya'yansu ba za su wadatar da su komai ba a wurin Allah; kuma wadannan su ne ma'abota wuta; suna masu dawwama a cikinta. --Quran/3/116
  2. Misalin abin da suke ciyarwa a wannan rayuwa ta duniya kamar misalin iska ce mai tsananin sanyi, sai ta auka kan shukar wadansu mutanen da suka zalunci kawunansu, sai ta lalata ta. Kuma Allah bai zalunce su ba, sai dai kawunansu suke zalunta. --Quran/3/117

Bayan da Allah ya ambaci siffofin wadanda suka yi imani daga cikin kafirai, sai kuma a wadancan ayoyi Allah ya bayyana siffofin kafirai da azabar da ya tanada musu a ranar Alkiyama, domin a gane bambancin da ke tsakanin mumini da kafiri. Allah ya bayyana cewa yawan dukiya da 'ya'ya da kafirai suke takama da shi a duniya, a wurin Allah ba zai wadatar da su komai ba, domin ba zai kare su daga azabar Allah ba; za a jefa su wutar Jahannama ne, su dawwama a cikinta har abada.

Kuma dukiyar da kafirai suke ta batarwa a nan duniya, da nufin yakar gaskiya da masu kira zuwa gareta, za su kashe ta ne a banza, domin ba za su taba cin nasara ba. Domin misalin wannan ta'asar da suke yi ta yi kama ne da wanda ya yi shuka, yana fatan samun amfaninta, sai wata guguwa mai karfi da sanyi ta taso ta halaka shukar gaba daya, bai tsira da komai ba daga amfaninta, kamar yadda Allah ya bayyana a Suratu Anfali, aya ta 36. Kuma wannan sakamako da Allah ya yi wa kafirai bai zalunce su da komai ba, suka zalunci kawunansu ta hanyar kafirci da fafutukar sai sun bice hasken Allah.

Daga wadannan ayoyi za mu fahimci abubuwa kamar haka:

  1. Sanin cikar ikon Allah, ta yadda babu wata hanya da kafirai za su iya bi su kare kansu daga azabarsa, komai yawan dukiyarsu da 'ya'yansu, domin ba za su tsinana musu komai ba a wajen Allah.
  2. Gargadi a kan guje wa ruduwa da yawan dukiya ko 'ya'ya. Domin wanda duk ya rudu da su; to ba zai saurari mai fada masa gaskiya ba, domin shi a ganinsa yawan dukiyar da aka ba shi ya ishe shi komai, don haka da wuya ya saurari gaskiya, ko ya nemi saninta.
  3. Ran mutum a wajensa amana ce Allah ya danka a hannunsa, don haka tilas ne ya kula da wannan amanar, kada ya aikata wani abu da zai cutar da ran nasa' idan har ya yi haka; to ya zama azzalumi.
  4. Allah Ta'ala ya kebance dukiya da 'ya'ya da ambato, domin su ne suka fi amfani ga mutum fiye da komai. Da dukiyarsa zai iya fansar kansa, ko ya kare kansa daga tafka asara; 'ya'ya kuma za su taimaka wa mahaifinsu, su ba shi kariya. To idan ya zamanto dan da mutum ya haifa ba zai iya tsinana masa komai ba, kuma dukiyar da yake da iko a kanta ba za ta yi masa wani amfani ba; to mene ne bayan su zai amfane shi, ya tsare shi daga kamun Ubangijinsa?

Tarjama Da Tafsirin ayoyin 118-120

  1. Ya ku wadanda suka yi imani, kada ku riki abokanan shawara wadanda ba a cikinku suke ba, ba za su sassauta muku mugunta ba, sun yi burin duk abin da zai kuntata muku, hakika kiyayya ta bayyana daga bakunansu; amma abin da zukatansu suke boyewa ya fi girma. Hakika Mun bayyana muku ayoyi; in kun kasance kuna hankalta. --Quran/3/118
  2. Sai ga shi ku dinnan kuna son su, su kuwa ba sa son ku, kuma ku kuna yin imani da Littattafai gaba dayansu, kuma idan sun gamu da ku, sai su ce: "Mun yi imani." Idan kuma sun kebanta, sai su rika cizon 'yan yatsu a kanku saboda bakin ciki. Ka ce: "Sai dai ku mutu da bakin cikinku." Lalle Allah Masanin abin da yake cikin kiraza ne. --Quran/3/119
  3. Idan wani kyakkyawan abu ya same ku sai ya bakanta musu rai, amma idan wani mummunan a ya same ku, sai su rika farin ciki da shi; amma idan kuka yi hakuri, kuma kuka yi takawa, makircinsu ba zai cutar da ku komai ba. Lalle Allah Yana kewaye da sanin abin da kuke aikatawa. --Quran/3/120 When you ˹believers˺ are touched with good, they grieve; but when you are afflicted with evil, they rejoice. ˹Yet,˺ if you are patient and mindful ˹of Allah˺, their schemes will not harm you in the least. Surely Allah is Fully Aware of what they do.

Tafsiri:

Bayan Allah SWT ya gama bayani a kan halayen muminai da na kafirai, sai kuma a wadannan ayoyi yake gargadin muminai da kada suna nuna musu asirinsu, su bar 'yan'uwansu muminai domin wadannan kadiran bai kamata a amince musu ba; duk sa'adda suka sami wata dama ta cutar da muminai; to sai sun yi amfani da ita. Kullum kuma suna jiran su ga muminai sun fada cikin wata wahala su kuma su samu abin yi musu dariya. Saboda tsananin kiyayyarsu ga muminai, har ta kai ba za su iya boye kiyayyar a zuciyarsu ba, sai su rika subutar baki suna fito da ita a fili, duk da haka kuma kiyayyar da ke cikin zukatansu ta fi girma fiye da wadda bakunansu suka furta har muminai suka ji. Allah ya bayyana ayoyinsa ga muminai a fili, kuma bayanin zai amfane su har idan sun saurare shi, sun kuma fahimce shi.

An karbo daga Abu Sa'id Alkhudiri (rA) ya ce,

Annabi SAW ya ce: "Babu wani annabi da Allah ya taba aiko shi, ko wani halifa da Allah ya ba shi halifanci, face yana da kashi biyu na masu ba shi shawara; kashin farko suna umartar sa da kyakkyawan aiki, suna kwadaitar da shi a kai; kashi na biyu kuwa suna umatarsa da sharri, kuma suna kwadaitar da shi a kan aikata shi. To tsararre shi ne wanda Allah ya tsare. [Bukhari #7198]

Narrated Abu Sa`id Al-Khudri:

The Prophet (ﷺ) said, "Allah never sends a prophet or gives the Caliphate to a Caliph but that he (the prophet or the Caliph) has two groups of advisors: A group advising him to do good and exhorts him to do it, and the other group advising him to do evil and exhorts him to do it. But the protected person (against such evil advisors) is the one protected by Allah.' " https://sunnah.com/bukhari:7198

Sannan Allah ya bayyana wani abu da ya wajaba muminai su yi hattara da shi dangane da sha'anin kafirai da munafukai; wannan abu kuwa shi ne saboda tsananin kiyayya da hassadar da ke cikin zukatansu ga muminai, ba za su taba jin suna son su a zukatansu ba. Su muminai kam suna nuna suna kaunar su su kuma kafitai ba sa son su, ba sa kuma kaunar su; tsakaninsu da su kiyayya ce kawai. Kamar yadda muminai suka yi imani da duk littattafan da Allah ya saukar wa annabawa, amma su kafirai na Yahudu da Nasara sun ki yin imani da abin da aka saukar ga Annabi SAW, bayan kuma sun jirkita nasu littattafan. To duk wanda irin wannan ne halinsa; to kamata ya yi a ki miyagun halayensu na munafirci, duk sa'adda za su hadu da muminai sai su rika nuna musu sun yi imani, amma kuma da zarar sun ware, sun kadaita da junansu, sai su rika cizon 'yan yatsunansu, saboda tsananin bakin ciki da haushin muminai, domin suna ganin irin hadin kan muminai da kaunar da ke tsakaninsu. Sai Allah ya umarci Annabinsa ya gaya musu: "Sai dai ku mutu da bakin cikinku" domin Allah ya yi alkawarin sai ya cika wannan ni'imar tasa, ya daukaka addininsa ko ba sa so, sai dai bakin ciki ya kashe su. Allah kuma yana sane da bin da yake boye a cikin kirazan bayinsa, don haka zai yi wa kowa sakayya a kan abin da ya aikata.

Sannan Allah ya bayyana abin da yake kara tsananin gabar kafiran ga muminai, watau duk lokacin da wani abin farin ciki ya sami muminai, sai su rika jin haushi, suna damuwa; yayin da kuma wani abin bakin ciki ya same su, sai su rika murna, suna jin dadi. Sai Allah ya koyar da muminai abin da zai taimaka musu wajen jure irin wannan hali na kafirai, watau su zama masu hakuri, kuma masu taqwa, domin idan har sun rungumi wadannan siffofi guda biyu, to babu wani makirci da zai cutar da su. Allah yana kewaye da saninsa game da abin da wadannan kafiran da munafukan suke yi, kuma zai saka musu a kan hakan.

Daga wadannan ayoyi za mu fahimci abubuwa kamar haka:

  1. Nisantar miyagun abokan shawara yana daga cikin imani, shi ya sa aka fuskantar da wannan maganar ga muminai.
  2. A nan an nuna ba kowa ne ya kamata ya zama abokin shawara ba. Idan an jarrabi mutum da mu'amala da makiya; to ya kamata mu'amalarsa ta kasance sama-sama, kada ya saki jiki ya rika buda masa sirrinsa, ko da kuwa zai rantse masa cewa yana son sa.
  3. Fadar Allah Ta'ala: "Sun so duk wani abu da zai kuntata muku..." yana nuna cewa, makiyammu suna son ganin duk abin da zai jefa mu cikin wahala, ya same mu; suna son ganin sun rushe mana tattalin arzikinmu da tsarin siyasarmu da zamantakewarmu, su kuma rusa mana addininmu, wanda samun haka shi ya fi komai muhimmanci a wurinsu.
  4. Aiki da luwa da amfani da hankali wajen la'akari da ayoyin Allah, shi ne hanyar samun ilimi da waywa.
  5. Duk sa'adda mutum ya zama mai zurfin hankali ne; to ya fi fahimtar ayoyin Allah.
  6. Gargadi ga muminai a kan haɗarin shugabantar da Yahudawa da Nasara a kan wani al'amarinsu na jagoranci. Domin su mutane ne da ba za su taƙaita ba wajen aikata wa Musulmi mugunta duk sanda suka samu dama. Kuma duk wani abin baƙin ciki da zai sami muminai to su za su yi farin ciki da shi ne; duk kuma wani abu na farin ciki da zai sami muminai to su baƙin ciki za su yi da shi. To irin waɗannan ta yaya muminai za su danƙa ragamar shugabancinsu a hannunsu?
  7. Maƙiyanmu ba za su gaji da shirya mana makirci da sharri ba; to maganin wannan kawai shi ne haƙuri da taƙawa. Mu yi haƙuri wajen aikata duk wani umarni da aka ba mu, da guje wa duk wani abu da aka hana mu. Duk wanda ya yi haƙuri ya ji tsoron Allah; to yana ƙarƙashin kulawar Ubangijinsa, babu makircin da zai cutar da shi.
  8. A ƙarƙashin aya ta 3:120, malamai suka fitar da ƙa'ida game da maƙiyi, suka ce shi ne wanda yake farin ciki da abin da ya baƙanta maka, yake baƙin ciki da abin da ya faranta maka. When you ˹believers˺ are touched with good, they grieve; but when you are afflicted with evil, they rejoice. ˹Yet,˺ if you are patient and mindful ˹of Allah˺, their schemes will not harm you in the least. Surely Allah is Fully Aware of what they do.

Tarjama Da Tafsirin ayoyin 121-129

  1. Kuma ka tuna lokacin da ka yi sammako daga wajen iyalinka, ka je kana shirya wa muminai wuraren tsayuwarsu don yaƙi. Allah kuwa Mai ji ne, Masani. --Quran/3/121
  2. Tuna lokacin da wadansu kungiyoyi guda biyu daga cikinku suka yi niyyar su ja da baya, amma Allah ne Majibincin lamarinsu. Sai muminai su dogara ga Allah kadai. --Quran/3/122
  3. Kuma tabbas hakika Allah Ya taimake ku a (yakin) Badar, alhalin kuna raunana, to ku ji tsoron Allah don ku zamanto masu godiya a gare Shi. --Quran/3/123
  4. Ka tuna lokacin da kake ce wa muminai: "Shin bai ishe ku ba idan Ubangijinku Ya kawo muku agajin mala'iku dubu uku wadanda za a saukar da su (daga sama). --Quran/3/124
  5. Haka ne, idan har za ku yi hakuri, kuma ku yi taqawa, kuma (kafirai) suka auko muku cikin gaggawa a wannan lokacin, to Ubangijinku zai ƙaro muku agaji da mala'iku dubu biyar masu alamomi. --Quran/3/125
  6. Kuma Allah bai sanya wannan ba sai don albishir a gare ku, kuma domin zukatanku su nutsu da shi. Kuma nasara ba ta zuwa daga kowa sai daga Allah Mabuwayi, Mai hikima. --Quran/3/126
  7. Domin Ya karya lagon wani bangare na kafirai ko Ya ƙasƙantar da su, sai su juya da baya suna taɓaɓɓu. --Quran/3/127
  8. Ba ka da komai cikin lamarin, ko dai (Allah) Ya karɓi tubansu, ko Ya yi musu azaba, lalle su dai azzalumai ne. --Quran/3/128
  9. Kuma abin da yake cikin sammai da kuma abin da yake cikin ƙasa na Allah ne. Yana yin gafara ga wanda Ya ga dama, Yana kuma yin azaba ga wanda Ya ga dama. Kuma Allah Mai gafara ne, Mai jin ƙai. --Quran/3/129

Tafsiri:

Bayan Allah SWT ya bayyana cewa hakuri da taqawa su ne makamin da mumini zai tsare kansa da shi daga cutarwar maƙiyansa,sai kuma a wadannan ayoyi Allah ya fito da bayanin abubuwan da kan sabbaba rashin samun nasara a kan maƙiya.

Allah yana tunatar da Annabinsa Muhammadu SAW lokacin da ya fito daga gidansa domin haduwa da kafiran Makka a ranar yakin Uhudu, lokacin da yake shirya rundunar muminai domin fita yaki, yana sanya kowa a muhallin da ya dace da shi. Domin Allah yana jin komai, yana jin shawarar da Annabi SAW ya yi da sahabbansa a kan wurin da ya kamata a yi wannan yaki. Kuma Allah shi ne masani dangane da ra'ayin da ya fi dacewa daga cikin ra'ayoyin da aka kawo a lokacin. Kuma yana sane da irin mugun nufin da kafirai da munafukai suka boye a zukatansu, har ma da abin da daukacin halittunsa suka boye a zukatansu.

Allah yana tunatar da Annabi SAW lokacin da wasu kungiyoyi biyu daga cikin muminai, suka yi nufin su janye daga wannan yaki, su ne kabilun Banu Salima da na Banu Harisa, sai dai kuma Allah ya kafe dugadugansu. Allah ya sanar wa Annabi SAW cewa, gare shi shi kadai ya wajaba muminai su dogara.

An karbo daga Jabir dan Abdullahi (rA) ya ce: A kanmu wannan ayar ta sauka:

"Ka tuna lokacin da wasu kungiyoyi biyu daga cikinku suka yi nufin su ja da baya, amma Allah ne majibincin lamarinsu..." Jabir ya ce: Mu ne kungiyoyin biyu, watau (i.e.) kabilar Banu Harisa da kabilar Banu Salima, kuma saukar da wannan ayar ya faranta mini rai, saboda fadarsa: "...amma Allah ne majibincin lamarinsu..." [Bukhari #4558]

Narrated Jabir bin `Abdullah:

The Verse:--

"When two parties from among you were about to lose heart, but Allah was their Protector," (3.122) was revealed concerning us, and we were the two parties, i.e. Banu Haritha and Banu Salama, and we do not wish (that it had not been revealed) or I would not have been pleased (if it had not been revealed), for Allah says:--"...Allah was their Protector."


Allah yana goranta wa muminai nasarar da ya ba su a ranar yakin Badar ne a yayin da suke 'yan kadan, masu rauni. Don haka ya dace su ji tsoron sa, su kiyaye dokokinsa, wala-alla su gode masa da baiwar da ya yi musu.

Sannan ya sake tunatar da Annabinsa Muhammad SAW, lokacin da yake yi wa sahabbansa albishir, yana cewa: "Shin ba zai ishe ku ba, Alla ya kawo muku dauki na mala'iku dubu uku (3,000), wadanda zai sauko da su daga sama su taya ku yaki?" To hakanan zai kawo muku tallafi idan har kun yi hakuri, kuma kun yi taqawa, kuma mushirkai sun bullo muku ta inda suka bullo cikin gaggawa.

Page 432

Sai Allah ya bayyana musu cewa, sanar da su da ya yi cewa, zai kawo musu agaji na mala'iku, wani albishir ne yake yi musu, domin su sami nutsuwar zukata. Daga karshe, nasara daga Allah take shi kadai, shi ne Mabuwayi, wanda ya fi karfin kowa, kuma mai hikima, zai ba su nasara ya kuma halakar da wasu kafiran, ko ya tozartar da wasu daga cikinsu, ya wulakanta su, daga karshe su koma garuruwansu a wulakance, ba tare da sun cim ma wata nasara ba. Ko kuma idan Allah SWT ya ga dama ya shiryar da su su musulunta, ko kuma ya yi musu azaba saboda zaluncinsu. Duk dai al'amauransu gaba daya suna komawa ne ga Allah, babu komai na al'amarinsu da yake a hannun wannan Annabi.

An karbo daga Anas dan Malik ya ce: An karya wa Annabi hakoransa na gaba ranar yakin Uhudu, aka kuma fasa masa kai, sai ya rika share jini daga jikinsa yana cewa: "Ta yaya mutanen da suka fasa kan Annabinsu, suka karya masa hakorinsa na gaba za su rabauta, alhalin yana kiran su zuwa ga Allah?" Sai Allah Ta'ala ya saukar da fadarsa: "Babu wani al'amari da yake hannunka..." [Muslim #1791]

It has been narrated on the authority of Anas that the Messenger of Allah (ﷺ) had his front teeth damaged on the day of the Battle of Uhud, and got a wound on his head. He was wiping the blood (from his face) and was saying:

How will these people attain salvation who have wounded their Prophet and broken his tooth while he called them towards God? At this time, God, the Exalted and Glorious, revealed the Verse:" Thou hast no authority" (iii. 127).

Sai kuma Allah ya tabbatar da cewa, shi kadai ne mai mulkin duk wani abu da yake sama, da wanda yake kasa, yana kuma yafe wa wanda ya ga damar yafe masa daga cikin bayinsa, ya kuma yi ukuba ga wanda ya ga damar yi masa ukuba, amma duk da haka shi mai yawan gafara ne, mai yawan rahama.

Daga wadannan ayoyi za mu fahimci abubuwa kamar haka:

  1. Kwarewar Annabi SAW wajen tsara sojojinsa a wurin yaki.
  2. Abu ne mai matukar muhimmanci ga jagoran mayaka, ya shirya mayakansa, kowanne ya nuna masa wurin tsayuwarsa da ya dace da shi, domin yin hakan yana daya daga cikin sabubban samun nasara a yaki.
  3. Kariya daga Allah take. Ba don wannan kariyar ba, da babu wanda zai kubuta daga aukawa cikin ramukan sabon Allah da zunubbai.
  4. Allah mai rufa asirin bayinsa ne masu laifi. Don haka a nan sai Allah bai fadi sunan kabilun da suka yi nufin janyewa daga fagen yaki tare da Annabi ba, kawai sai ya ce 'wadansu kungiyoyi biyu'. God conceals the faults of His slaves... hence why He didn't specify which exact groups.
  5. Allah mai tausaya wa bawansa ne, sai ya nefe shi da tsayawa da jajircewa a kan gaskiya.
  6. Wajabcin dogara ga Allah; yin haka yana daga cikin imani da Allah.
  7. Ya wajaba ga Musulmi ya sama wa kansa kariya daga duk wani abin ki, ta hanyar dogoro ga Allah, ka da ya zama mai raki.
  8. Taqawa tana daga cikin hanyoyin gode wa Allah; ita ce Musulmi zai sanya ta zama katanga tsakaninsa da azabar Allah, watau dai ya aikata abin da aka wajabta masa, ya kuma bar abin da aka haramta masa. Wannan kuwa shi ne hakikanin godiya ga Allah.
  9. Duk sa'adda bawa ya fi nuna kaskancinsa ga Allah, to ya fi kusa da samun nasararsa. A duk kuma lokacin da bawa yake nuna tsarsa, to lokacin ne yake rasa samun taimakon Allah a gare shi.
  10. Bayanin irin kyakkyawar mu'amalar Manzon Allah SAW ga sahabbansa lokacin da suke fuskantar wata fargaba da tashin hankali. Annabi SAW yakan shigar musu da kyakkyawan fata a zukatansu, wanda hakan shi ne yakan dawo musu da kuzarinsu, ya tafiyar musu da bakin cikinsu da damuwarsu, ya sa su tashi tsaye domin aiki ba ja da baya.
  11. Sama ita ce mazaunin mala'iku, sai dai sau tari sukan sauko kasa da umarni Allah.
  12. Allah yakan ba wa muminai nasara a kan kafirai, domin ya rage mugun iri, ba don ya halaka duk ilahirin kafirai ba. Saboda yana daga cikin hikimar Allah, ya bar imani da kfafirci su ci gaba da wanzuwa, suna ta qaruwa, domin tantance mumini na gaskiya da wanda ba na gaskiya ba.
  13. Cewar da Allah ya yi, al'amari ba a hannun Annabi yake ba, don haka ba ya halattun Ubangiji ba mallakinsa ne ba, don haka ba ya halatta mumini ya roke shi, ko ya nemi agajinsa da taimakonsa a kan abin da ba mai yin sa sai Allah, ballantana kuma wani waliyyi.
  14. Annabi SAW shi ma bawa ne na Allah, kuma har ya bar duniya yana karbar umarni da hani ne daga Allah. Da wannan ne za mu fahinci batan masu da'awar cewa, akwai wasu waliyyai da suke kaiwa matakin da sun fi karfin su karbi umarni ko hani daga Allah, ko kuma bawa ya kai wani matakin da shari'a take sauka daga kansa. Wannan kafirci ne, ba Musulunci ba.
  15. Allah yakan yi wa kafirai azabar da babu hannun wani Musulmi a ciki.

Tarjama Da Tafsirin Aya Ta (130-132)

  1. Ya ku wadanda suka yi imani, kada ku ci riba ninki-ba-ninkin, kuma ku ji tsoron Allah don ku rabauta. --Quran/3/130
  2. Kuma