Toggle menu
24K
665
183
158.2K
HausaDictionary.com | Hausa English Translations
Toggle preferences menu
Toggle personal menu
Not logged in
Your IP address will be publicly visible if you make any edits.

voa60/2020-12-07

From HausaDictionary.com | Hausa English Translations

VOA60 World for Monday (Litinin) Dec 7th, 2020

English [1] Hausa [2] [3]

  1. VOA60 World for Monday (Litinin) Dec 7th, 2020 [4]
    1. Indonesia: Six suspected supporters of hardline Islamic cleric Muhammad Rizieq Shihab were killed in a clash with police on Monday, Jakarta police said.
      A Indonesia, an kashe wasu magoya bayan wani malami mai tsattsauran ra'ayi, su shidda, a arangama da 'yan sanda a cewar 'yan sandan Jakarta. --voa60/2020-12-07

    2. Ghana: The 12 candidates for president, including those believed to be the frontrunners, cast their ballots in the presidential election Monday. They included President Nana Addo Dankwa Akufo-Addo and former President John Dramani Mahama.
      'Yan ƙasar Ghana, sun kada ƙuri'a a zaɓen shugaban ƙasa, inda hankali yafi karkata akan batun tattalin arziƙi, yayin da ƙasar ta fuskanci komaɗar tattalin arziki a karon farko cikin kusan shekaru arba'in. --voa60/2020-12-07

    3. Britain: Post-Brexit trade talks hung in the balance as Britain and the European Union made a last-minute attempt to bridge significant differences and reach a deal that would avoid a disorderly exit in just 24 days.
      Tattaunawa tsakanin Burtaniya da Tarayyar Turai, game da makomar dangantakar su idan Burtaniya ta fice daga ƙungiyar, tana tangal-tangal, yayin da ɓangarorin biyu ke neman mafita nan da kwana ashirin da biyu. --voa60/2020-12-07

    4. Venezuela: President Nicolas Maduro on Monday hailed a "gigantic electoral victory" for his Socialist Party following parliamentary elections over the weekend, in a vote marred by an opposition boycott and low turnout. Opposition leader Juan Guaido has described the vote as a “fraud.”
      Shugaba Nicolas Maduro na Venezuela, ya yaba da babbar nasarar da jam'iyyar shi da 'yan gurguzu ta samu a zaɓen 'yan majalisar dokoki, wanda 'yan adawa suka ƙauracemawa --voa60/2020-12-07

    5. New Zealand: Prime Minister Jacinda Ardern vowed accountability for the families of last year's Christchurch mosque attack victims, ahead of the public release of a major report into the country's worst massacre.
      Firam minastan New Zealand Jacinda Arden, ta sha alwashin tabbatar da adalci da iyalan mutanen da aka kashe a harin masallaci na Christchurch a bara. --voa60/2020-12-07