Overview
- Lesson Title: Reconciliation-This is an excerpt from a 2014 radio interview about the possibility of reconciliation between Boko Haram and the Nigerian government. WinXP users should install Arial Unicode font.
- Language: Hausa
- Topic: Defense/Security
- ILR Level: 2+/3
- ACTFL Proficiency: Superior, Advanced-High; This ACTFL rating is an approximation based on the ILR level
- Modality: Listening
- Learning Objective: Maintenance & Improvement
- Subject Area: Language
- Material Type: LLO
- Publication Year: 2015
- ObjectID: c14lhau01
Transcript
Original | Translation |
---|---|
BARISTA TANIMU KABIRU TURAKI: Gwamnati tana son a yi maganin wa’yannan abubuwa da suka adabi ƙasan nan. Kuma Lillahiwa Rasulihi idan har ana so a yi magani wanda zai kasance an yi wa tufka hanci, to tilas ne gwamnati ta ɗauki matakan yin duka abun da ya kamata a yi. Ya kasance an samu zaman lafiya dawamamme. Amma, abinda ya kamata a fahimta a ko yaushe, idan ma gwamnati ta ce za ta yadda a kai ga matsayin ba ni gishiri in baka manda, to, da wa za’a zauna? Domin abubuwan da muka cigaba da samu a baya, ba abubuwa ne wanda su ke bamu ƙarfin gwiwa cewa, idan ma har an yarda an yi abun da su ke buƙata ai masu, cewa to to, za’a samu sauƙi a wannan ba. Zan ba da misalai: A da, ana cewa, ba za’a yi sulhu ba sai an saki yara da mata waɗanda aka kama suke hannun jami’an tsaro na gwamnati. Ta hanyar kwamitin sulhu muka sa Shugaban Ƙasa ya ba da umurni, jami’an tsaro suka saki mata, suka saki yara ƙanana, kuma, a cikin matan nan da aka saka, akwai matar Shekau a ciki. Mun san matarsa ce, amma aka sake ta. Akwai kanwar Shekau, mun san cewa ƙanwarsa ce. Aka sake ta. Amma, me ya faru da ga baya? Wannan ya kawo biyan buƙata? Kwaliya ba ta biya kuɗin sabulu ba. To, shi ne muke cewa tun da gwamnati ta kafa: kwamiti na ci gaba da sulhu, to idan dai wannan ne tsakani da Allah ne ake magana wannan bayani da suke yi, to, su zo, mu a shirye muke a, kwammiti na sulhu, mu zauna da su, a tattauna duk abubuwan da suke akan tebur, har ma da wannan maganar yaran nan, ‘yan matannan da aka sace, na Chibok, a zauna a ga ta wace hanya ne za’a bi a sa mu dawamammen zaman lafiya? Wannan shi ne bayanin da muke, a ko yaushe. Abunda shi Shekau yake bayani shi ne cewa, ku sakar musu mutanensu, su kuma, su sakar muku wa’yannan yara. Shin gwamnati tana da tunanin yin haka? BARISTA TANIMU KABIRU TURAKI: Ai, na ba ka misali a baya, cewa an ce a saki mata da yara, mun sake su, ce wa su ma za su cika alƙawari. Sun cika nasu alkawari? Amma, tunda ba mutumin da muka zo muka ce: Kai wane, ga wa’yannan nan mutanen mun baka su, kai kuma muna buƙatar ka yi kaza, to, ba’a samu cika alƙawari ba. Saboda haka, ai magana ce ta sulhu, to already, gwamnati ta sa kwamitin sulhu, yana nan, yana aikinsa. A ko yaushe, aka zo aka tattauna da wannan, sai a ce ai ba’a bashi dama ya wakilci ƙungiya ba. To, shi ne mu a kwamitin sulhu mu ke cewa: Idan dai wannan zancen da suke faɗa gaskiya ne, Imamu Abubakar Shekau, ya fito ya ce ga waƙilan Jama’atul Ahlalsunna Dil-altul wuji ya waɗanda za’a zauna a yi magana da su. In an yi haka, mu kwamitin sulhu, za mu zauna da su, za mu fara tauttaunawa akan duk abunda yake ba kawai maganar 'yan matan chibok ɗin nan ba. To, mu a kwamitin, a shirye muke ko ina ma suke so, ba sai cikin Nijeriya ba. KABIR YUSUF: Ba ka jin, suna tsoron kada su turo wakilansu a kamasu, shi ya sa suke ƙin fito da waɗannan? BARISTA TANIMU KABIRU TURAKI: Duk mutumin da zai zo yin sulhu, ba za’a kamashi ba, mun bada garanti cewa zai zo lafiya, zai koma lafiya. Kuma, za mu cika wannan alkawarin. |
BARRISTER TANIMU KABIRU TURAKI: The government wants to find a solution to these things that are troubling this country. Also, truthfully speaking, if they want a lasting solution to settle this matter, the government must take the responsibility to fulfill everything that is required so that lasting peace is achieved. However, what we need to always understand is even if the government says they agree to reach the point of negotiations, well, who are they going to sit with? Because the outcomes we kept getting from them were not encouraging enough, so that if we were to agree and do what they want us to do, this time around things will get better. I am going to give an example. Previously, they said there would be no reconciliation until the children and women [affiliated with Boko Haram— Trans .] who were arrested by government security officials are released. We made the president give instructions through the reconciliation committee, and security officials released the women and they also released the little children. Shekau’s wife was one of the women who were released. We knew it was his wife, but they released her. There was also Shekau’s sister and we knew it was his sister. But they released her. But what happened later on? Did this bring satisfaction? The end did not justify the means. Thus, we concluded that since the government has established the reconciliation committee, well, if indeed what they [Boko Haram— Trans .] say is sincere, then they can come and the reconciliation committee is ready to sit with them to discuss all the issues on the table, including the talk about these children, the young girls that were kidnapped from Chibok, to sit and find out what methods to follow to achieve lasting peace. This is what we are saying, always. KABIR YUSUF: What Shekau is saying is that you should release his people, and then they too will release these girls to you. I wonder, is the government thinking about doing this? BARRISTER TANIMU KABIRU TURAKI: Well, I gave the example earlier that if we release the women and children, they [Boko Haram— Trans .] will fulfill their promise. Did they fulfill their promise? But we didn’t arrive in person to say, “You there, here are these people, we give them to you; we also require that you do this or that.” Hence, they didn’t fulfill their promise. Because of that, it is a matter of reconciliation, and already the government has set up a reconciliation committee, it exists and it is working. Whenever the government talks with someone, they will say he was not given the permission to represent the organization. Hence, we at the reconciliation committee declared that, if indeed this dialogue that they speak of is true, Imam Abubakar Shekau should come out and appoint representatives of the Party of the People of the Sunna who will attend the talks. If they do this, we are the reconciliation committee, we will sit with them, we will start discussing everything that there is to discuss, and not just the issue of the Chibok girls. Well, we at the committee, we are ready anywhere they want, not necessarily within Nigeria. KABIR YUSUF: Don’t you think they are afraid to send a representative because they fear he will be arrested? That is why they are refusing to come out for this? BARRISTER TANIMU KABIRU TURAKI: Anyone who comes for reconciliation will not be arrested; we guarantee that he will arrive safely and go back safely. We will fulfill this promise. |
Glossary
- Lillahiwa Rasulihi (lit: for the sake of God and His messenger) truthfully speaking
- yi wa tufka hanci (lit: loop at the end of a rope) settle this matter
- ba ni gishiri in baka manda (lit: you give me salt and I give you money) negotiations
- ƙarfin gwiwa (lit: strength of the knee) encouraging
- Kwaliya ba ta biya kuɗin sabulu ba (lit: the facial does not reflect the value of the soap) the end did not justify the means
- Jama’atul Ahlalsunna Dil-altul wuji Party of the People of the Sunna (from Arabic)
- Another version of this item is Jama'atu Ahlis Sunna Lidda'Awati Wal-Jihad ‘people committed to the Prophet’s teachings for propagation and jihad’, and it is the official name of Boko Haram. The word sunna refers to Muslim law, based on Muhammad’s words or acts, that are accepted as authoritative by Sunni Muslims.
Notes
The Notes provide cultural and linguistic information helpful for comprehending the text. Boko Haram Boko Haram is an Islamic political group based in Nigeria. Founded in 2002 by a group of Islamic clerics in the Nigerian state of Borno, its first leader was Mohammed Yusuf. Boko Haram has sought to impose Sharia law throughout all of Nigeria. The group was non-violent until 2009, when it refused to comply with a law that required motorcyclists to wear helmets. More than 800 people were killed in the ensuing riot between Boko Haram and the police (Ford 2014). Since then, Boko Haram has become increasingly violent, and it was designated a terrorist group by the United States in 2013 (Abubakar 2014). In April 2014, members of Boko Haram kidnapped nearly 300 schoolgirls in Chibok, prompting an international outcry. As of early 2015, Boko Haram controls territory in the northeastern Nigerian states of Yobe, Adamawa, and Borno, particularly in the area surrounding Maiduguri, the capital of Borno and the city in which Boko Haram was founded (Ashkenas et al. 2014). Abubakar, Abdullahi Tasiu. May 9, 2014. "Nigeria's Boko Haram Leader Abubakar Shekau in Profile." BBC. http://www.bbc.com/news/world-africa-18020349. Ashkenas, Jeremy, Derek Watkins, and Archie Tse. December 11, 2014. "Boko Haram: The Other Islamic State." New York Times. http://www.nytimes.com/interactive/2014/12/11/world/africa/boko-haram-nigeria-maps.html. Ford, John. June 6, 2014. "The Origins of Boko Haram." The National Interest. http://nationalinterest.org/feature/the-origins-boko-haram-10609. Imam Abubakar Shekau As of 2014, Abubakar Shekau is the leader of Boko Haram, having assumed this role following the death of Mohammed Yusuf in 2009. Shekau has not been seen in public since 2009, but since then has released a series of videos and still images online to make his presence known (Abubakar 2014). Since Shekau's ascension, Boko Haram's actions have become increasingly violent (Abubakar 2014). Abubakar, Abdullah Tasiu. May 9, 2014. "Nigeria's Boko Haram Leader Abubakar Shekau in Profile." BBC. http://www.bbc.com/news/world-africa-18020349.