Toggle menu
24K
665
183
158.2K
HausaDictionary.com | Hausa English Translations
Toggle preferences menu
Toggle personal menu
Not logged in
Your IP address will be publicly visible if you make any edits.

bbchausa/EndSars20 Oktoba 2020

From HausaDictionary.com | Hausa English Translations

https://www.bbc.com/hausa/labarai-54622806

EndSars: Ƴan sanda sun buɗe wa dubban masu zanga-zanga wuta a Legas

20 Oktoba 2020

Ana fargabar mutane da dama sun mutu bayan sojoji sun buɗe wa dubban masu zanga-zangar EndSars wuta a dandalin Lekki toll gate da ke birnin Legas a kudancin Najeriya da yammacin Talata.

Masu zanga-zangar sun ci gaba da yin ta ne bayan da gwamnatin jihar ta sanya dokar hana fita ta sa'a 24 a jihar a ranar Talata da safe sakamakon ƙona wani ofishin yan sanda da aka yi.

BBC tana cikin nuna bidiyon ci gaban zanga-zangar kai tsaye a shafinta na Facebook a lokacin da aka fara harbe-harbe da bindiga a wajen.

Dubban mutane ne suka sake taruwa a dandalin na Lekki toll gate suna ci gaba da zanga-zangar.

Amma nan da nan sai komai ya hargitse wajen ya cuɗe. Babu tabbas kan ko mutum nawa ne suka jikkata a lamarin wanda ya faru da misalin ƙarfe 6.45 na yamma agogon Najeriya.

Sannan babu bayanai a hukumance kan alkaluman mutane da suka mutu ko jikkata. Sai dai wani ganau ya tabbatar wa BBC cewa ya ƙidaya gawawwaki 20 an kuma jikkata sama da 50.

Tuni dai zanga-zangar ta rikiɗe zuwa rikici tsakanin masu yin ta da wasu da ake zargin ƴan daba ne a wasu manyan biranen ƙasar da suka haɗa da babban birnin tarayya Abuja.

Shi ma wakilin sashen BBC Pidgin ya ce ya ga mutum ɗaya da ya jikkata.

Rahotanni na nuna cewa ƴan sandan kwantar da tarzomar sun yi ƙawanya sun zagaye masu zanga-zangar da suka ƙi guduwa.

Kuma sauran waɗanda suka rage ba su gudu ɗin ba sun haƙiƙance cewa za su ci gaba da zanga-zangar EndSars ɗin.

A yanzu gwamnan Legas Babajide Sanwo-Olu ya bayar da umarnin cewa ka da a fara aiki da dokar hana fitar sai ƙarfe 9 na daren yau saboda mutanen da cunkoson ababen hawa ya rutsa da su su samu damar koma wa gida.

Sojojin sun fara harba harsasai sama ne da farko, su kuma masu zanga-zangar suka fara amfani da abin wasan wuta don mayar wa sojojin martani, a cewar wakilin BBC Pidgin da ke wajen.

Wasu masu zanga-zangar dai suna cewa mutane sun mutu wasu kuma sun jikkata bayan faruwar lamarin.

Amma har yanzu rundunar sojin Njeriya ba ta ce komai ba.

Dama tun da farko a ranar Talatar Babban Sifeton 'yan sandan Najeriya ya umarci baza 'ƴan sandan kwantar da tarzoma a duk faɗin ƙasar.

Sanarwar Muhammad Adamu, na zuwa ne yayin da ake samun ƙaruwar tashin hankali a wasu jihohi sakamakon zanga-zangar nuna adawa da cin zalin da ake zargin jami'an 'yan sanda na yi.

Tuni a wasu jihohin ma aka sanya dokar hana fita ta sa'a 24 kamar Jos da Ekiti da Abia.

https://www.bbc.com/hausa/labarai-54625203

EndSars: Jihohin Najeriya da zanga-zanga ta rikiɗe zuwa tarzoma

Minti 1 da ta wuce

Gwamnonin jihohi da dama a Najeriya sun sanya dokar hana fita ta tsawon sa'oi 24 sakamakon rikiɗewar da zanga-zangar SARS ta yi zuwa tarzoma.

Gwamnonin wadanan jihohi sun ce sun sanya dokar hana fita ne sakamakon yadda ɓata-gari ke amfani da damar zanga-zangar SARS wajen haifar da rikici da kai hare-hare.

Ga jihohin Najeriya da aka ƙaƙaba wa dokar hana fita saboda zanga-zangar #EndSARS

KANO

Zanga-zanga ta zama rikici a Kano tsakanin masu zanga-zanga da wasu 'ƴan daba.

'Yan dabar ne suka fara kai wa masu zanga-zangar hari a dai-dai makarantar horas da sojojin sama a can hanyar filin jirgin sama na malam Aminu, sun tarwatsa masu zanga-zanga tare da yi musu duka da sare-sare, an kuma kashe mutum 2 a cewar masu zanga-zangar.

Hakan ya tunzura su suka rufe hanyar da za ta kai ka Sarkin Yaki a unguwar Sabon Gari. Daga nan su ma suka dauko makamai da katakwaye da adduna suka tare hanya suka kona tayoyi.

An kona motoci 2 da farfasa wasu da dama an kuma fasa kantin cin abinci na Chicken republic amma 'yan sanda sun tseratar da ma'aikatan wajen.

A yanzu dai lamarin ya lafa, amma ana ci gaba da zaman dar-dar a yankin Sabon Gari. Kuma ba a sanya dokar hana fita a jihar ba.

Me ke faruwa a sauran sassan ƙasar?

Tun da farko a ranar Talata Babban Sifeton 'ƴan sandan Najeriya ya umarci baza 'ƴan sandan kwantar da tarzoma a duk faɗin ƙasar.

Sanarwar Muhammad Adamu, na zuwa ne yayin da ake samun ƙaruwar tashin hankali a wasu jihohi sakamakon zanga-zangar nuna adawa da cin zalin da ake zargin jami'an 'yan sanda na yi.