Baqara 1-5
- Alif Lam Mim. --Quran/2/1
- Wannan littafi ne da babu wani kokwanto a cikinsa; shiriya ne ga masu taqawa. --Quran/2/2
- Wadanda suke yin imani da abin da galibi kuma suke tsayar da salla kuma suke ciyarwa daga abin da Muka azurta su da shi. --Quran/2/3
- Wadanda suke yin imani da abin da aka saukar maka da abin da aka saukar a gabaninka, kuma suke sakankancewa da ranar lahira. --Quran/2/4
- Wadannan suna kan (babbar) shiriya daga Ubangijinsu, kuma wadannan su ne masu samun babban rabo. --Quran/2/5
Tafsiri:
Allah swt ya bud'e wannan Sura da harufin Alif da Lam da Mim. Ban da ita wannan Sura da akwai surorin Alqur'ani da dama da Allah ya bud'e su da irin wadannan haruffa. Da dama daga cikin malamai suna cewa, Allah ne kad'ai ya san abin da yake nufi da su (only Allah knows the meaning of these disjointed letters). Wasu kuma sun yi qoqarin bayyana ma'anoninsu. Amma magana mafi inganci ita ce, Allah yana nuna mu'ujizar AlQur'ani ne ta hanyar ambaton wadannan haruffa. Domin suna tabbatar wa larabawa cewa babu wanda zai iya kawo wani abu irin Alqur'ani, duk kuwa da cewa haruffansa su ne haruffan da suke magana da rubutu da su.
Allah ya siffanta wannan Alqur'ani da cewa, babu wani kokwanto a cikinsa,
- Allah describes this Quran as having no doubt in it,
wato duk abin da ya qunsa tabbatacce ne kuma gaskiya ne,
- that is, everything it contains is certain and true,
don haka ne ya zama shiriya ga masu taqwa,
yana nuna musu gaskiya da bayyana musu hukunce-hukunce wad'anda suka shafi aqidunsu da ibadunsu da kuma mu'amalolinsu.
- showing them the truth and explaining to them the rulings that affect their beliefs, their worship, and their dealings.
An kira Alqur'ani da sunan Littafi duk kuwa da kasancewarsa ba a tattara shi wuri guda ba a lokacin;
- The Quran was called the Book, even though it was not collected in one place at the time;
an yi haka ne domin a yi ishara zuwa ga cewa, nan gaba za a tattara shi wuri guda ya zama littafi wanda Musulmi a kowane lokaci za su riqa karantawa.
- This was done to indicate that in the future it would be collected in one place and it will become a book that Muslims would read at all times.
Sannan Allah swt yana fayyace siffofin masu taqwa wadanda Alqur'ani yake shiryar da su.
- Then Allah (swt) describes the characteristics of the pious people whom the Quran guides.
Sun siffantu da siffofi guda biyar kamar haka: <> They are described with five characteristics as follows:
- Suna yin imani da gaibu. Gaibu shi ne duk abin da manzanni suka zo da shi, suka ba da labarinsa, kuma ido bai gan shi ba. Wannan ya had'a da imani da ranar lahira da abin da ta ƙunsa na hisabi da mala'iku da labarin manzanni da littafan da Allah ya saukar gabanin zuwan Manzon Allah swt. Imani da gaibu shi ne yake bambance wa tsakanin mutum mumini da kafiri, saboda yana imani da duk wani abu da Allah ya ba da labarinsa ko Manzonsa ya fad'a ko da kuwa bai gano shi da hankalinsa ba.
- They believe in the unseen. The unseen is everything that the messengers brought, reported, and the eye has not seen. This includes belief in the Day of Judgment and what it entails, the angels, the stories of the prophets, and the books that Allah revealed before the coming of the Messenger of Allah (swt). Belief in the unseen is what distinguishes a believer from a disbeliever, because he believes in everything that Allah has reported or His Messenger has said, even if he does not understand it with his own mind.
- Suna tsayar da salla, wato suna yin ta kamar yadda shari'a ta koyar da su tare da kula da lokutanta da rukunanta da wajibanta da sharuɗɗanta.
- Suna ciyar da abin da Allah ya azurta su da shi. Sukan fitar da zakkar dukiyoyinsu, hakanan suna sadaka ta nafila da abin da Allah ya hore musu.
- Su ne waɗanda suke yin imani da Alƙur'anin da Allah ya saukar wa Annabi Muhammadu (SAW) gaba ɗaya ba tare da ware ɓangare ko sun riƙa tawilin karkatar da ma'anonin wani ɓangare na Alƙur'ani ba, kamar yadda 'yan bidi'a suke yi ga wasu ayoyin waɗanda ba sa goyon bayan bidi'o'insu da aƙidunsu. Hakanan suna yin imani da dukkan littattafan da Allah ya saukar wa manzanni da annabawan da suka gabata, har da su kansu manzannin da annabawan.
- Su ne waɗanda suka tabbatar da zuwan ranar tashin alƙiyama da abubuwan da za ta zo da su na tayar da matattu da yi musu hisabi da suka wa mutanen ƙwarai da Aljanna; masu miyagun laifuffuka kuwa a saka musu da wutar Jahannama. An ware batun imani da ranar lahira duk kuwa da cewa ya shiga cikin batun imani da gaibu, saboda a zaburar da mutane ga ayyukan alheri a kuma tsoratar da su game da munanan ayyuka.
Sannan Allah swt ya faɗi sakamakon masu waɗannan siffofi da cewa, suna kan wata shiriya mai girma daga Allah mai yi musu tarbiya ta ƙwarai. Domin babu wata shiriya da ta kai siffantuwa da waɗannan siffofi. Don haka su ne waɗannan suke da babban rabo daga Allah, wato samun yardar Allah da gidan Aljanna ranar gobe alƙiyama.
Daga waɗannan ayoyi za mu fahimci abubuwa kamar haka:
- Girman mu'ujizar Alƙur'ani.
- Allah swt ya yi ishara zuwa ga cewa, za a tattara Alƙur'ani wuri guda don ya zama littafin da Musulmi za su riƙa ɗauka suna karantawa a kowane zamani.
- Alƙur'ani shiriya ne ga mutane masu taqwa. Watau masu kiyaye dokokin Allah. Gwargwadon taƙawar bawa gwargwadon yadda zai dace da shiriyar Alqur'ani. Wanda kuma ya rungume shi yana aiki da shi to babu shakka shiriyarsa za ta riƙa hauhawa tana ƙaruwa.
- Duk abin da Alqur'ani ya qunsa gaskiya ne babu kokwanto ko kad'an a cikinsa.
- Falalar yin imani da gaibu, domin shi ne abin da yake buqatar qarfin imani, sab'anin abin da kowa yake iya gani ko yake iya ji, wannan abu ne da babu mai iya musanta samuwarsa.
- Girman sha'anin tsai da salla, domin ita ce rukuni na biyu daga cikin rukunan Musulunci.
- Falalar ciyar da dukiya don Allah.
- Siffar masu taqawa ta ƙunshi bauta wa mahalicci ba kyautata wa mahluki.
- Imani da duk littattafan da Allah swt ya saukar wa manzanninsa, domin sanin cewa Allah swt bai bar bayinsa hakanan sakaka ba tare da bayyana musu hanyar shiriya ba.
- Shiriya da rabauta ba za su taɓa samuwa ga bawa ba sai ya rungumi wannan hanyar, ya siffantu da waɗannan siffofi.
Baqara 6-7
- Lalle waɗanda suka kafirta, duk ɗaya ne a gare su, ka yi musu gargaɗi ko ba ka yi musu ba, ba za su yi imani ba. --Quran/2/6
- Allah Ya toshe zukatansu da jinsu, kuma akwai wani lulluɓi a kan idanunsu, kuma suna da azaba mai girma. --Quran/2/7
Tafsiri:
A nan Allah yana ba da labarin kafirai ne da irin taurin kansu wajen kafirce wa abin da Annabi SAW ya zo da shi na gaskiya.
- Here, Allah is telling the story of the disbelievers and their stubbornness in rejecting what the Prophet (peace and blessings of Allaah be upon him) brought as truth.
Allah
pg18