Toggle menu
24K
665
183
158.2K
HausaDictionary.com | Hausa English Translations
Toggle preferences menu
Toggle personal menu
Not logged in
Your IP address will be publicly visible if you make any edits.

Quran/18/archive

From HausaDictionary.com | Hausa English Translations

1. Sura ta 18

  1. Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, Wanda ya saukar da Littafi ga bawanSa, kuma Bai saka masa karkata ba.
  2. Ya yi shi madaidaici, don ya yi gargadin azaba mai tsanani daga gare Shi, kuma ya yi bushara ga waɗanda ke Yin ayyuka nagari, cewa suna da kyakkyawan sakamako.
  3. Da za su zauna cikinsa har abada.
  4. Ku ma don ya gargaɗi waɗanda suka ce, ‘Allah ya riƙi ɗa’.
  5. Su ko iyayensu ba su da sani game da haka. Kalmar da ke fita daga bakunan-su ta munana. Babu abin da suke faɗa, sai ƙarya.
  6. Mai yiwuwa ne baƙin ciki ya kashe ka (don jiye musu takaici) idan ba su ba da gaskiya da wannan zance ba.
  7. Hakika, Mun sa dukkan abin da ke ban ƙasa, ya zama ado gare ta, don Mu jarraba su Mu ga ko wanne a cikinsu zai fi yin aiki nagari.
  8. Kuma za Mu mai da abin da ke kan ta, ya zama faƙo.
  9. Ko ka taɓa tunanin cewa, Mazauna kogo Marubuta Allo ababan ta’ajibi ne daga cikin AyoyinMu?
  10. Lokacin da waɗannan samarin suka nemi mafaka cikin kogo, suka ce, ‘Ubangijin mu, Ka bamu rahama daga wajenKa, kuma Ka agaza mana da shiriya game da al'amarin mu.’
  11. Sai Muka hana kunnuwansu ji, har zuwa shekaru masu yawa, a cikin kogon.
  12. Sa’annan Muka tashe su, don Mu san wanene daga cikin ƙungiyoyin biyu zai fi kiyaye tsawon lokacin da suka zauna.
  13. Mu za Mu ba ka labarinsu na gaskiya. Su samari ne, waɗanda suka ba da gaskiya da Ubangijinsu, kuma Mun ƙara masu shiriya.
  14. Kuma Mun ƙarfafa zukatansu, lokacin da suka miƙe tsaye, suka ce,‘Ubangijinmu ne Ubangijin sammai da ƙasa. Ba za mu taɓa kira wani ubangiji ba, sai Shi; (idan muka kira wani ba Shi ba), mun furta magana ta zautuwa.
  15. Waɗannan mutanenmu sun riƙi wasu abubuwan bautawa bayanSa. Me yasa ba su kawo ƙwaƙkwaran dalili game da su ba?’ Kuma wanene mafi zalunci da yafi mai ƙirƙiro ƙarya game da Allah?
  16. Kuma yayin da kuka ƙaurace musu, da abin da suke bauta wa maimakon Allah, ku fake cikin kogo; Ubangijinku zai shimfiɗa maku rahama taSa, kuma Zai agaza maku da sauƙi game da lamarinku.
  17. Kuma yayin da rana ta fito, za ka gan ta tana kauce wa kogonsu ta hannun dama, kuma idan ta fadi, za ka gan ta tana juya musu baya ta hannun hagu; su kuwa suna cikin fili mai fadi a cikinsa. Wannan yana daga Ayoyin Allah. Wanda Allah ya shiriya, shi ne shiryayye; wanda Ya bari bisa ɓata kuwa, ba za ka sama masa mai agaji, mai shiryarwa ba.
  18. Za ka zaci a farke suke, alhali barci suke; Kuma za Mu sa su su juya dama kuma su juya hagu, karensu kuwa ya miƙe ƙafafuwansa na gaba kan dokin ƙofar. Idan ka hange su, sai ka juya musu baya a firgice, kuma sai ka cika da jin tsoronsu.
  19. Kuma sai Muka tashe su, don su tambayi junansu. Mai magana a cikinsu ya ce, ‘Menene tsawon zamanku?’ Suka ce, ‘Mun zauna rana ɗaya, ko kuma sashin rana,’ wasu suka ce, ‘Ubangijinku ne ya fi sanin tsawon zamanku. Ku aiki ɗayanku da wannan kuɗinku na azurfa naku, ya je birni; ya duba wanda ya fi abinci mai kyau, ya kawo muku abinci daga can, kuma ya yi halin kirki, kuma kada ya sanar da kowa game da ku’.
  20. ‘Don su in suka rinjaye ku, za su jefe ku, ko kuma su mai da ku cikin addininsu, idan haka ta faru, ba za ku rabauta ba, har abada.
  21. Ta haka Muka nuna su (ga mutane), don su san cewa alƙawarin Allah gaskiya ne, kuma tsayuwar Sa’a babu kokwanto game da ita. (Tuna) yayin da mutane suke jayayya game da lamarinsu a tsakaninsu, sai suka ce, ‘Ku tada gini a kansu; Ubangijinsu ne ya fi saninsu.’ Waɗanda suka fi galaba a jayayyar suka ce, ‘Haƙiƙa, za mu gina ɗakin ibada a kan su.’
  22. Waɗansu za su ce, ‘Su uku ne, karensu ne na huɗu ɗinsu;’ waɗansu kuma za su ce, ‘Su biyar ne, karensu ne na shidansu;’ suna safci-faɗi. Kuma waɗansu na cewa, ‘Su bakwai ne, karensu ne na takwas ɗmsu.’ Ce, ‘Ubangijina ya fi kowa sanin yawansu. Babu wanda ya san su sai kaɗan.’ To, kada ka yi jayayya game da su, sai fa jayayya mai hujja, kuma kada ka nemi labarinsu daga kowa daga cikinsu.
  23. Kuma game da kowane abu, kada kace, ‘Zan yi wannan gobe.’
  24. Sai fa idan Allah ne ya so. Kuma idan ka manta, tuna Ubangijinka, kuma ka ce, ‘Ina fata Ubangijina ya ɗora ni kan hanyar da ta fi wannan kusantar gaskiya. ’
  25. Sun zauna cikin kogonsu shekara ɗari uku, kuma sun ƙara tara akai.
  26. Ce, ‘Allah ne ya fi sanin tsawon zamansu.’ Sanin sirrin cikin sammai da ƙasa naSa ne. Gani sai Shi, kuma ji sai Shi. Banda Shi, ba su da wani mai taimako, Shi kuma ba ya tarayya da wani a cikin hukuncinSa.
  27. Kuma karanta abin da aka yi maka wahayi cikin littafin Ubangijinka. Babu wanda zai iya canja kalmominSa. Babu mai mafaka, sai gare Shi.
  28. Kuma ka shaƙu da waɗanda ke kiran Ubangijinsu, safe da yamma, suna masu neman yarda taSa; kuma kada idanuwanka su wuce kansu, kana mai haƙon samun ƙawan rayuwar duniya; kuma kada ka biye wa wanda Muka rafkanar da zuciyarsa daga ambatonMu, kuma ya bi son zuciyarsa, kuma lamarinsa ya kauce (daga hanya mai kyau).
  29. Kuma ce, ‘Wannan gaskiya ne daga ubangijinku; to, wanda yaso, ya yarda kuma wanda ya so, ya ƙi yarda.’ Mu kuwa Mun tanada wa masu laifi Wuta, runfunanta za su mamaye su. Idan suka yi kukan neman taimako, za a taimake su da ruwa mai kamar narkakken darma, wanda zai riƙa ƙona fuskokinsu. Wannan abin sha ya munana, kuma wannan mazauni ya ƙuntata.
  30. Haƙiƙa, waɗanda suka ba da gaskiya, kuma suka yi ayyuka nagari, Mu, ba ma tozarta sakamakon waɗanda suka kyautata aiki.
  31. Waɗannan suna da Lambuna na Dauwama. Koramu na gudana ƙarƙashinsu. A ciki za a yi masu ado da mundaye na zinari, kuma za su saka tufafi koraye, na siliki na ainihi da karam miski, suna kishingiɗe a kan kujeru. Wannan sakamako ya yi kyau, kuma wannan mazauni ya dace!
  32. Kuma ba su misali na mutum biyu; Mun ba ɗayansu lanbuna biyu na inabai, kuma Mun kewaye su da bishiyoyin dabino, kuma a tsakaninsu mun saka gonakin hatsi.
  33. Dukkan lambunan biyu sun yi ‘ya’ya (birjik), kuma ba su tauye komai ba. Kuma Mun sa ƙorama na 6ul6ulowa a tsakiyarsu.
  34. (Don haka) ‘ya’yan itatuwa (masu yawa) sun samu gare shi. Sai ya ce wa abokinsa, yana jayayya da shi, ‘Na fi ka yawan dukiya kuma na fi ka ƙarfin jama’a.’
  35. Kuma ya shiga lambunsa yana mai zaluntar kansa. Ya ce, “Ba na zato wannan gonar za ta ƙare har abada.
  36. Kuma ba na zato Ranar Kiyama mai wanzuwa ce, kuma idan ma aka mai da ni gurin Ubangijina, zan sami makomar da ta fi wannan kyau.”
  37. Abokinsa yana jayayya da shi, ya ce masa. “Shin ka kafirce wa Wanda ya halicce ka daga turɓaya, sa’annan daga digon maniyyi. Sa’annan ya baka sura ka zama (cikakken ) mutum
  38. Amma (ni), Allah, Shi ne Ubangijina, kuma ba zan yi wa Ubangijina tarayya da kowa ba.
  39. Lokacin da ka shiga lambunka me ya hana ka ce Abin da Allah ya so ne kawai zai faru. Babu wani mai ƙarfi sai Allah, idan kana ganin na fi ƙarancin dukiya da ‘ya’ya.
  40. Mai yiwuwa ne, Ubangijina ya ba ni abin da ya fi gonarka. Ko kuma ya sako mata tsawa daga sama, sai ta wayi gari taɓo mai santsi.
  41. Ko kuma ruwan ya ƙafe kuma ba za ka iya tono shi ba.”
  42. Sai aka halakar da ‘ya’yan itatuwan nasa, sai ya wayi gari yana juya tafukansa, don baƙin cikin abin da ya ɓatar a kanta, ita kuwa ta rushe, runfiinanta akwance, ya riƙa cewa, ‘Kaicona, ina ma ban yi wa Ubangijina tarayya da wani ba! ’
  43. Kuma ba shi da jama’ar da za ta taimake shi, banda Allah, kuma ba zai iya taimakon kansa ba.
  44. A irin haka, taimako yana gurin Allah ne kawai, Ubangiji na Gaskiya. Shi ne mafificin ba da sakamako, kuma shi ne mafificin kawo ƙarshe nagari.
  45. Kuma ba su misalin rayuwar duniya: Ita kamar ruwa ne da muka saukar daga sama, sai shuke-shuken ƙasa suka cuɗanya da shi, daga baya ya zama ciyayi wanda iska ke watsarwa. Kuma Allah Mai iko ne bisa komai.
  46. Dukiya da ‘ya’ya, su ne adon rayuwar duniya. Ayyuka nagari kuwa, su ne mafifita a gurin Ubangijinka, don biyan buƙatan yanzu, kuma su ne mafifita , don biyan buƙatan nan gaba.
  47. Kuma (tuna) ranar da za Mu kawar da duwatsu, kuma zaka ga mutanen ban ƙasa suna tunkuɗar juna, kuma za Mu tara su gaba ɗaya, ba za Mu bar kowa ba daga cikinsu.
  48. Kuma za a kawo su gaban Ubangijinka, safu-safu; (Zai ce musu), ‘Ga ku kun zo gurinMu yadda Muka halicce ku tun farko. Da can kuwa kun zaci ba za Mu cika alƙawarin da Muka yi muku ba.’
  49. Kuma za a ajiye Littafin (ayyuka gabansu), sai ka ga masu laifi suna tsoron abin da lce cikinsa, kuma za su ce, ‘Kaiconmu, me ya sa wannan Littafi, ba ya barin ƙaramin aiki ko babba, sai ya rubuce shi. ’ Kuma za su sami abin da suka aikata na jiran su, kuma Ubangijinka ba zai cuci kowa ba.
  50. Kuma (tuna lokacin ) da Muka ce wa mala’iku, ‘Ku miƙa wuya ga Adama.’ Sai suka miƙa wuya, banda Iblis. Wanda ke cikin aljanu, shi ya ƙi bin umamin Ubangijinsa. To, kwa riƙe shi, da zuriyarsa masoya maimakoNa, alhali su maƙiyanku ne? Canjin masu laifi ya munana.
  51. Kuma Ban maida su shaidun halittar sammai da ƙasa ba,ko halittar kansu, kuma ba na riƙon masu taimako daga masu ɓatarwa.
  52. Kuma tuna ranar da zai ce, ‘Kira abokan tarayya nawa.’ Sai su kira su, amma ba za su amsa ba, kuma sai Mu saka kariya a tsakaninsu.
  53. Kuma masu laifi za su ga wuta, su kuma san cikinta za su faɗa, kuma ba mafita daga gareta.
  54. Kuma haƙiƙa Mun yi bayani ta hanya daban-daban da misali iri-iri ga mutane a cikin wannan Kur’ani, amma mutun ya fi kowane abu yawan gardama.
  55. Kuma ba wani abu ya hana mutane su ba da gaskiya ba, yayin da shiriya ta zo kuma su nemi gafara gurin ubangijinSu, sai don jiran sakamakon mutanen farko ta zo musu, ko kuma azaba ta zo musu ƙuru-ƙuru.
  56. Kuma ba Ma aiko Manzanni sai don su yi bushara da gargadi. Kuma waɗanda suka kafirta suna jayayya da ƙarya, don su karya gaskiya da ita. Kuma sun ɗauki AyoyiNa da gargaɗin da aka yi musu abin yi wa izgili.
  57. Wanene mazalunci fiye da wanda aka yi masa gargaɗi da Ayoyin Ubangijinsa amma ya bijire musu, kuma ya manta abin da hannuwansa suka gabatar. Mu, Mun saka marufai (yana) kan zukatansu,don kada su fahimce shi, kuma Mun saka nauyi cikin kunnuwansu. Don haka ba za su karɓa ba har abada ko ka kira su zuwa shiriya.
  58. Kuma Ubangijinka Mai gafara, ne, Ma’abucin rahama. In da Zai kama su bisa abin da suka aikata, sai Ya gaggauta musu da azaba. Amma suna da lokaci ƙayyadadde da ba za su sami mafaka daga gare shi ba.
  59. Kuma waɗannan garuruwa Mun halakar da su, yayin da suka yi laifi, amma Mun ƙayyade lokacin halakar da su.
  60. Kuma (tuna) lokacin da Musa ya ce wa abokinsa saurayi. ‘Ba zan gushe ba ina tafiya, sai na isa mahaɗar teku biyu, ko kuma in ci gaba da tafiya shekaru aru-aru.’
  61. Amma yayin da suka isa mahaɗar tsakaninsu (tekuna biyu), sai suka manta kifinsu, sai ya kama hanyarsa yana gudu a cikin teku.
  62. Kuma bayan sun tsallake wannan gurin,sai yace wa abokinsa saurayi, ‘Kawo mana abincinmu, haƙiƙa, mun haɗu da wahala a wannan tafiyar tamu.’
  63. Ya ce, baka gani ba, lokacin da muke hutawa kan dutse, na manto kifm, kuma Shaiɗan ne kawai ya mantar da ni in ambata maka, sai ya yi wuf, ya faɗa cikin teku, abu ya bani mamaki.’
  64. Ya ce, ‘Abin da muke nema ke nan.’ Sai suka juya baya, suna bin sawun ƙafafuwansu.
  65. Sai suka tarar da wani bawa daga cikin bayinMu da Muka ba wa rahama daga wajenMu, kuma Muka sanar da shi sani daga wajenMu.
  66. Musa ya ce masa, ‘Zan iya bin ka,don ka koya mini shiriya daga abin da aka sanar da kai?’
  67. Ya ce, ‘ Ba za ka iya haƙuri da ni ba.’
  68. ‘Yaya kuwa za ka iya haƙuri, a kan abin da ba ka fahimce shi ba?’
  69. Ya ce, ‘In Allah ya so za ka same ni mai haƙuri, kuma ba zan saɓa wa umaminka ba. ’
  70. Ya ce, ‘To, idan za ka bi ni, kada ka tambaye ni game da wani abu, sai na yi maka bayani game da shi.’
  71. Sai suka tafi, sai can suka shiga jirgin mwa sai ya huda shi, ya ce, ‘Ka huda shi don ka sa mutanen cikinsa su nitse? Gaskiya ka yi abu mai haɗari.’
  72. Ya ce, ‘Ban faɗa maka ba cewa,ba za ka iya haƙuri da ni ba?’
  73. Ya ce, ‘Kada ka riƙe ni bisa abin da na manta,kuma kada ka kyare ni da tsanani bisa mantuwa da na yi.’
  74. Sai suka ci gaba dai,sai can suka haɗu da wani yaro,sai ya kashe shi. Ya ce, ‘Ka kashe mai rai wanda bai yi laifin komai ba, ba tare da ya kashe mai rai ba? Haƙiƙa, ka aikata abu mai muni.’
  75. Ya ce, ‘Ban faɗa maka ba cewa,ba za ka yi haƙuri da ni ba?’
  76. Ya ce, ‘Idan na sake tambayar ka game da wani abu, kada ka abuce ni, haƙiƙa ka kai matuƙa game da karɓar hanzari daga gare ni.’
  77. Sai suka tafi dai, har suka isa gun mutanen wani gari, suka nemi abinci gurin mutanen garin, sai suka ƙi karbar baƙuncinsu. Sai suka tarar da wani garu yana neman faɗuwa, sai ya miƙar da shi. Ya ce, ‘Da ka so, sai ka karɓi lada a kan wannan aikin.’
  78. Ya ce, “Wannan ne maraba tsakanina da kai. Zan faɗa maka ma’anar abin da ka kasa haƙuri game da shi.
  79. Jirgin nan, na wasu talakawa ne da ke aiki cikin teku. Sai na yi niyyar ɓata shi, don akwai sarki a bayan su, da ke ƙwace duk wani jirgi mai kyau.
  80. Yaro kuwa, iyayensa su biyu muminai ne. Sai muka tsoraci ya masife su da shishshigi da kafirci.
  81. Sai muka yi fatar Ubangijinsu ya canja masu wanda ya fi shi tsarki da kusancin jinƙai.
  82. Garu kuwa na wasu yara ne marayu su biyu a bimin, kuma a ƙarƙashinsa akwai taskar dukiya mallakinsu, ubansu kuma ya kasance managarci. Sai Ubangijinka ya nufi sukai ƙarfmsu, kuma su fitar da taskar dukiyarsu, don jinƙai daga Ubangijinka. Ban yi dukkan wannan bisa ra’ayina ba. Wannan ne ma’anar abin da ka kasa haƙuri game da shi.”
  83. Kuma suna tambayarka game da Zulƙamaini. Ce, ‘Zan faɗa maku tarihi game da shi.’
  84. Mu, Muka gina shi a ƙasa, kuma Mun ba shi hanyar samun kowane abu.
  85. Sai ya bi wata hanyar.
  86. Har ya isa mafaɗar rana ya same ta kamar tana faɗuwar cikin idon mwa mai taɓo. Kuma ya tarar da mutane a gurin. Muka ce, ‘Ya Zulƙamaini, ko dai ka azabtar da su, ko kuma ka yi masu nasiha.’
  87. Ya ce, ‘Wanda ya yi laifi, za mu azabtar da shi, sa’annan za a mai da shi gurin Ubangijinsa, Wanda zai yi masa horo da azaba mai tsanani.’
  88. Amma wanda ya bada gaskiya kuma yayi aiki na gari zai sami sakamako mai kyau, kuma za Mu yi masa magana mai sauƙi da furucinMu.
  89. Sa’annan ya bi wata hanyar.
  90. Har ya isa mafitar rana, ya same ta tana fitowa kan wasu mutane, da ba Mu yi musu kariya daga gare ta ba.
  91. Haka abin ya faru. Kuma Muna da cikakken sanin abin da ke tare da shi.
  92. Sa’annan ya bi wata hanyar.
  93. Har ya isa fili fayau tsakanin tsaunuka biyu. Ya tarar da wasu mutane ƙarƙashinsu, ba sa iya fahimtar maganarsa sosai.
  94. Suka ce, ‘Ya kai Zulƙamaini, haƙiƙa, Yajuju da Majuju maɓamata ne a ƙasa. Ko mu ba ka lada, don ka kafa mana kariya tsakaninmu da su?’
  95. Ya ce, ‘Karfin da Ubangijina ya ba ni ya fi (ladar da za ku bani). Amma ku taimake ni da leburori masu ƙarfi, zan yi bango tsakaninku da su.’
  96. Ku kawo mini tubalai na ƙarfe. Sai da ya cike filin da ke tsakanin gefen tsaunukan biyu, ya ce, ‘Ku hura (da zuga-zugai). Sai da ya mai da shi ja kamar wuta, ya ce, ku kawo mini narkakken tagulla don in zuba a kansa’.
  97. Daga nan, Yajuju da Majuju ba su iya tsallaka shi ba, kuma ba su iya huda shi ba.
  98. Ya ce, ‘Wannan rahama ce daga Ubangijina. Amma idan alƙawarin Ubangijina ya zo, Zai mai da shi msashshe, alƙawarin Ubangijina kuwa gaskiya ne.’
  99. A wannan rana za Mu bar sashinsu su kara da sashi. Kuma za a busa ƙaho. Sa’annan Mu tara su gaba ɗaya.
  100. Kuma a wannan rana, za Mu kawo wa kafirai Jahannama suna ganinta.
  101. Waɗanda idanuwansu suka rufe basa sauraran tunatarwaNa, kuma ba ma za su iya jin zancen gaskiya ba.
  102. Shin waɗanda suka kafirta suna zato, za su riƙi bayiNa abin dogara maimakoNa? Haƙiƙa, Mun tanadar wa kafirai Jahannama ta zama masaukinsu.
  103. Ce, ‘Ba Ma ba ku labarin waɗanda suka fi taɓewa game da ^ ayyukansu ba?’ 105. Su ne waɗanda suka ɓace, sun duƙufa kan rayuwar duniya kawai, kuma suna zato kyakkyawan aiki suke.
  104. Waɗannan su ne suka kafirce wa Ayoyin Ubangijinsu, da kuma haɗuwa da Shi, sai ayyukansu suka ɓaci. A ranar Kiyama, ba za Mu ɗauke su bakin komai ba.
  105. Haka ne sakamakonsu- Jahannama, don sun kafirce, kuma sun ɗauki AyoyiNa da ManzanniNa abin yi wa izgili.
  106. Haƙiƙa, waɗanda suka ba da gaskiya, kuma suka yi ayyuka nagari,
  107. Gidajen Aljanna na Firdausi ne masaukin su.
  108. Za su dauwama a cikinta, ba za su nemi a fidda su daga ita ba.
  109. Ce, ‘Idan dukkan mwan teku ya zama tawada don mbuta kalmomin Ubangijina, sai tekun ya ƙare kafin kalmomin Ubangijina su ƙare, ko Mun kawo wani tekun kamarsa, ƙari.’
  110. Ce, ‘Ni mutum ne kamarku. Amrna anyi mini wahayi cewa, Ubangijinku, Ubangiji ne Daya. To, wanda ke ƙaunar saduwa da Ubangijinsa, ya yi aiki nagari, kuma kada ya tara wani cikin bautar Ubangijinsa.’